Popular posts from this blog
ATIKU YA GANA DA WAKILAN CIBIYAR KASA DA KASA TA REPUBLICAN DA CIBIYAR HARKOKIN DIMUKURADIYYA TA KASA, AN BADA SHAWARAR SAMAR DA TAKARDUN ZABE DA ZASU KAWAR DA SIYAN KURI'U
Dan Takarar shugabancin Najeriya a Jam'iyyar PDP a zabe Mai zuwa Alh. Atiku Abubakar (GCON) ya yi wata ganawa yau a Abuja da wani ayarin hadin gwiwa daga cibiyar kasa da kasa ta republican da cibiyar harkokin demukuradiyya ta kasa NDI karkashin jagorancin Mr. Frank LaRose sakataren jihar Ohio ta Amurka. Wannan dai yana kumshe ne a cikin takardar bayan taro, wadda Mataimaki na Musamman ga Alh. Atiku Abubakar din kan Kafofin Watsa Labarai AbdulRasheed Shehu ya fitar. A taron, Wazirin Adamawa yace ya yi ganawa Mai muhimmancin gaske da ayarin, dangane da muhimmancin alfanun bunkasa dimukuradiyyar gaskiya a tsarin gudanar da zabe Musamman kare tsarin doka da oda da sauran batutuwa. Tsohon mataimakin shugaban kasar ta Najeriya yace a yayin tattaunawar tasu, ya bada shawarar Samar da takardun zabe na Musamman domin kawar da matsalar sayen kuri'u Wanda ke Neman zama ruwan dare a tsarin zabukan mu. A karshe taron, Dan Takarar ta PDP ya godewa bakin
ATIKU YA SHA ALWASHIN TABBATAR DA DAIDAITUWAR TATTALIN ARZIKIN NAJERIYA YAYIN YAKIN NEMAN ZABEN SA GOMBE
Dan Takarar shugabancin Najeriya na Jam'iyyar PDP a zaben badi Alhaji Atiku Abubakar yayin yakin neman zaben sa a Gombe ya yi alkawarin daidaita tattalin arzikin Najeriya idan aka zabe shi badi. Da yake jawabi ga dandanzon magoya bayan sa da shugabannin Jam'iyya da jagorori a filin wasa na Gombe, tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi alkawarin aiki domin inganta tattalin arzikin Najeriya da ci gaban ta. Ya bawa mutanen Gambe tabbacin cewar gwamnatin sa zata farfado da Dam din Dadin Kowa inda ya yi kira ga mutanen jihar su bashi dama ya zama Tafawa Balewa na biyu, inda yace an shafe Lokaci Mai tsawo yankin Bai Samar da shugaban Najeriya ba. Atiku ya ce zuwa Gombe kamar zuwa gida ne a wurin sa, ya kuma bada tabbacin warware matsalar tsaro a yankin tare da maido da zaman lafiya sannan ya farfado da tattalin arziki a dukkan matakai. Masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar PDP a jihar ta Gombe sun bada tabbacin goyon baya ga Atiku da Jam'iyyar sa. Da suke ma
Comments
Post a Comment